Iddar wadda mijinta ya rasu ya bart...

Egypt's Dar Al-Ifta

Iddar wadda mijinta ya rasu ya barta

Tambaya

Mene ne iddar matar da mijinta ya rasu ya barta? Shin ya halatta ta fita a lokacin da take idda?

Amsa

Iddar matar da mijinta ya rasu ya barta shi ne watanni hudu da kwana goma, a lissafin kamariyya (Hijira); saboda ayar da Allah Madaukakin Sarki ya ce: (Su kuwa wadanda suka rasu daga cikinku suka bar mata, za su tsahirta ga barin yin aure har na tsawon watanni hudu da kwanaki goma) [al- Bakra: 234].

Ya halatta ta fita daga gidan aurenta a yini, tare da la’akari da ta rika kwana a gidan aurenta a duka lokacin iddarta.

Allah Madaukakin Sarki shi ne masani.

Share this:

Related Fatwas