Shafa fatiha bayan addu’a

Egypt's Dar Al-Ifta

Shafa fatiha bayan addu’a

Tambaya

Mene ne hukuncin shafan fuska da hannu bayan kamala yin addu’a, domin akwai wadanda suke bayyana hakan a amtsayin bidi’a wacce ake kinta?

Amsa

Yana daga cikin sunnah daukaka hannaye biyu a lokacin yin addu’a, tare da shafan fuska da su bayan kammala yin addu’an bayan yin sallah ko a wajenta, akan wannan fahimtar jumhor din malamai suka tsaya akai.

Allah ya umurcemu da yin addu’a sannan ya yi mana alakawarin amsa mana, Allah Mai girma ya ce:(Sai Ubangijinku ya ce ku rokeni zan amsa muku) [Gafir:60], yana daga cikin sunnonin da ake son aikatawa a lokacin yin addu’a daga hannaye, sannan a ashafi fuska da su hannayen bayan kammala sallah ko a wajenta, akan wannan akayu ittifaki tare da halascinsa a wurin Hanafiyya da Shafi’iyya da Hanabila, saboda fadin Manzon Allah sallallaHu AlaiHi wa AliHi Wasallam: (Idan za ku roki Allah to ku rokeshi da tafin hannuwanku, kada ku rokeshi da bayan hannunku, sannan ku shafa fusakunku da hannayenku) Hakeem.

Share this:

Related Fatwas