Ambaton Allah a kowane yanayi

Egypt's Dar Al-Ifta

Ambaton Allah a kowane yanayi

Tambaya

Shin ya halatta a yi tasbihi da zikiri a lokacin da mutum yake cikin janaba?

Amsa

Zikiri shi ne ibadar da Allah Madaukakin Sarki ya yalwata lokacinta da sharuddanta da ma yanayinta, ana son a yi a kowane irin hali, da lokaci ba tare da kaidi da halin cikakken tsarki ko waninsa ba; an bayar da umurnin a yi zikiri ne mudlaki, wannan sai ya nuna cewa ya halatta a yi zikiri a kowane irin yanayi mutum ya sami kansa a ciki; Allah Madaukakin sarki ya ce: (Ya ku wadanda kuka yi imani, ku ambaci Allah da Ambato mai yawa. Ku kuma tsarkake shi safiya da maraice) [al- Ahzab: 41- 42], haka ma Allah Madaukakin Sarki ya ce: (Lallai a cikin halittar da Allah ya yi wa sammai da ƙasa, da abubuwan da suke cikin su na ƙwarewa da gwaninta, da saɓanin da dare da rana suke da shi, na haske da duhu, tsawo da gajerta, akwai bayyanannun ayoyin ga masu hakalin da suke iya riskar kaɗaitakar Allah da ikon sa. Shi kuwa sha'anin masu hankali –a koda yaushe- shi ne su halarto da girman Allah da buwayan sa cikin zukatan su, a kuma duk inda suke, shin suna tsaye ne, ko a zaune, ko a kwance, suna tunani akan halittar sammai da ƙasa, da abubuwan da suke cikin su na ban mamaki, suna cewa: ya Ubangijin mu, lallai ba ka halicci waɗannan abubuwa ba sai domin hikimar da ka hukunta, kai ka tsarkaka ga barin tawaya, a'a, ka halicce su ne domin su zamo dalilai da za su yi nuni akan ikon ka, su kuma zamo alamu ne da za su nuna isar hikimar ka; saboda haka, ya Ubangiji ka tsare mu ga barin azabar wuta, ta hanyar katartad da mu zuwa ga hanyar yi maka biyayya) [Ali Imran: 191- 192].

Lallai Annabi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam) yana ambaton Allah a dukan yanayin da yake ciki (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam); an ruwaito Hadisi daga Sayyida A’isha Ummul’muminina (Allah ya kara yarda da ita) ta ce: (Manzon Allah (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam) yana ambaton Allah a dukan yanayin da yake ciki) [Muslim].

Imam Alnawawiy ya ruwaito ijma’in malamai akan halaccin yin zikiri da harshe ga mutumin da yake cikin janaba, da mai al’ada da mai jinin biki; a cikin littafinsa “al- Azkar: 11” [Malamai sun yi ijma’i akan halaccin yin zikiri da harshe ga mutumin da yake cikin janaba, da mai al’ada da mai jinin biki, kaman tasbihi da tahlili da tahmidi da takbiri da salatin Annabi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam) da addu’a da sauransu].

Allah shi ne masani.

Share this:

Related Fatwas