Kiyaye rai
Tambaya
Ta yaya musulunci ya bukaci kare mutum da zaman lafiyarsa?
Amsa
Addinin musulunci ya bukaci kare mutum daga dukkan abin da zai iya cutar da shi, sai ya sanya kare martaban mutum daga cikin manufofin shari’a na bai daya wanda dukanin hukunce hukunce su ka zo domin tabbatar da hakan, daga baya wadannan manufofin suka hauhawa har suka kai ga matsayin wajibi, shari’ar bayyananniya ba ta tsaya kan kare hakkin mutum ba kawai a cikin rayuwarsa da amincin kansa, a,a ta wajabta masa bin matakan da hanyoyin da za su kare martabansa na rayuwarsa da lafiyar jikinsa ta kare shi daga illa da cutuwa.
Alamomin kiran da musulunci ya yi kan kare martaban mutum su na da yawan gaske, daga ciki akwai : umurni da neman magani da kuma rigakafi daga cututtuka, daga ciki akwai hana kashe ran da ba a yi umurni da kasheta ba, tare da yin horo mai tsauri ga wanda ke aikata hakan, har wala yau daga cikin haka akwai hana cutar da kai ko wani, daga Abu Sa’ed Al’khudri Allah ya kara masa yarda ya ce: Annabi S.A.W. ya ce: (Babu cuta ba cutarwa) Hakeem ne ya ruwaito.